KUNGIYAR GAMAYYAR KUNGIYOYIN YAN SHIA TA NAJERIYA, TAREDA MABIYA DA MASOYA AHLULBAYT, NA JIHAR KANO SUNYI GAGARUMIN TARO DON BAYYANA IRIN ĎAN TAKARAR DA ZASU ZAƁA, A WANNAN ZAƁEN DA YA TUNKARO.
A jiya Talata 21/2/2023, ne mabiya Shi'a, da wasu kungiyoyin Sharifa, da wani bangare na Ashabul Kahfi, da sauran kungiyoyin da suke karkashin "AHLULBAYT NIGERIA" reshen jihar kano, suka yi gangami a Rufaffen Ďankin Taro na, filin wasa na Sani Abacha, da ke kofar Mata Kano, domin kara bayyanawa duniya cewar sun shirya tsaf domin shiga a dama dasu, kuma su jefa quri'unsu a dunkule, ga wani ayyanannan Ďan takara, tun daga matakin Shugabancin Kasa, har zuwa matakin Karamar Hukuma, a zaben wannan sharakarar ta 2023.
Harwa yau, a wannan taron Shugaban Gamayyar na qasa, wato Hon. Garba Ya'u Gwarmai, ya bayar da Tallafi na jari ga mutane 300, inda aka baiwa Mata 100 naira N10,000 kowacce, sai kuma ya bayarda N5000 ga mutane 200 mata da maza.
Wannan taron ya sami halartar dimbin membobin wannan wannan kungiya, da kuma wakilcin wasu bangarorin.
A wannan taron Shugaban Gamayyar ta qasa, wata Hon. Garba Ya'u Gwarmai ya bayyanawa mahalarta taron maqasudin kiran wannan gangami, tareda shelanta cewar, "zamuyi za6e a wannan shekara, kuma zamu haďu dukkaninmi, kwanmu da kwarkwatarmu, mu marawa wani ďankara ďaya tilo, muyi masa ruwan quri'armu a dunkule, wanda muke ganin ya cancanta, kuma zai ďaukemu kamar kowanne ďan kasa, ba tare da banbanta mu da kowa ba. Kuma zuwa yanzu bamu kai ga bayyana ďan takarar da zamu za6a ba a dukkan matakai, amma zamu bayyana muku ďan takarar da zamu marawa bayawa a cikin kwanaki biyu masu zuwa"
A nashi 6angaren jawabin, shima Shugaban Gamayyar na jihar Kano Alhaji Adamu Kabiru Audua ya bayyana cewar "Zamu dunkule quri'unmu wuri guda, mu tuttulawa ďan takara guda a dukkan matakai, kuma muna da sharaďin za6ar kowanne ďan takara, kuma sharaďin baya nufin a bamu fifiko, ko a banbantamu, ko a bamu wani abu kafin muyi za6e. Sharaďin mu kawai shine ayi mana adalci, a ďauke mu kamar kowanne ďan kasa, kuma mu amfani gwamnati kamar yadda kowanne ďan kasa yake amfana.
Wannan taron ya sami halartar manyan Malamai daga 6angarorin Shia, Ashabul Kahfi, Tijjaniyya, da sauran 6angarorin da ake wannan tafiya tare.
Sannan kuma taro ya sami halartar Mawaqa, da suka hadarda Dr. Aminu Abubakar Ladan (ALA), Malam Bashir Ďandago da sauran mawaqa da dama.
![](https://i.ytimg.com/vi/3w4kr3yxxxM/maxresdefault.jpg)