*ALLÃH YAYI WA SANI GARBA SK RASUWA*
*Fitacce kuma jajirtaccen Jarumin fina finan Hausa na Kannywood Sani Garba SK ya rasu a ranar Laraba 15 ga watan Disamba 2021 a birnin kano bayan ya sha fama da rashin lafiya.*
Sanarwar ta fito ne kai tsaye daga wajen wani fitaccen furodusa kuma jigo a masana'antar kannywood wato Abdul M Amart Mai Kwashewa.
Amart ya fitar da sanarwar jim kadan bayan mutuwar marigayin a yammacin Laraba, Allãh Ya Karbi ran marigayin ne a wani babban asibiti Mai suna Muhammadu Abdullahi Wase dake Nassarawa.
"Sani Garba SK ya sami a kalla shekara uku ko fiye ma da haka yana fama da rashin lafiyar amma a tsaitsaye, inda a baya bayannan ne kuma cutar ta sake taso masa inda ya shafe tsawon mako biyar yana jinya a dai wannan asibitin" cewar Abdul Amart.
Abdul Amart ya kara da cewa "tun asali cutar ciwon suga ce yake fama da ita inda daga bisani ta haifar masa da wasu nau'o'in cututtuka na daban, kamar ciwon koda da kuma ciwon hanta da kuma hawan jini.
Tun a baya dai an sha yada jita-jitar rasuwar Sani Garba SK inda a wasu lokutan yakan fito ya musanta da kansa yana mai tabbatarwa da mutane cewa " shi fa duk wani mai rai mamaci ne komai dadewa, mutuwa tana kan kowa, tare da adu'ar Allãh Ya sa mu cika da imani idan ta zo.
Abul M Amart Mai Kwashewa dai shine wanda ya dauki bauyin yi masa maganin inda a ranar da aka fara masa aikin ne ya riga mu gidan gaskiya.
Sani Garba SK dai dan asalin Unguwar Zage ne dake cikin birnin Kano dake Arewacin Nijeriya. Kafin ya shiga harkar fim, Sani Garba SK ya kasance sha'iri ne na yabon Fiyayyen Halitta (S.A.W) a kungiyar Usha'un Nabiyyu.
Ance kafin kwanciyar sa a asibitin Nassarawa dai da ya kwanta a asibitin Murtala dake birnin na Kano.
An kuma yi masa jina'iza ne a ranar Alhamis 16 ga watan Disamba 2021.
Allãh Ya Garfarta Masa ya kuma kyautata namu
Ещё видео!