Jawabi akan hukuncin azumin sit Shawwal by Dr Sani Umar Rijiyar Lemo
YARO TSAYA MATSAYIN KA KADA ZANCEN YAN DUNIYA YA RUƊE KA.
Dr. Gumi ya zama fitina ga Musulmi
✍ Dr. Aliyu Muhammad Sani
Sabanin da Dr. Ahmad Gumi yake yi da Al'ummar Musulmi a kan Azumin Sittu Shawwal sabani ne mai sauki fa! Saboda shi Dr. Gumi bai dora ra'ayinsa a kan Manhaja ta ilmi ba. Kawai ya dora ne bisa makauniyar biyayya ga Imamu Malik, ta yadda yake ganin Addini kawai shi ne abin da Imamu Malik ya fada, duk abin da Malik ya ajiye to Bidi'a ne a Addini.
To ka ga wannan ba Manhaja ce ta ilimi ba, Manhaja ce ta Ta'assubanci a Addini. Saboda ba dole ne sai an bi Imamu Malik ba, don Allah bai aiko mana Imamu Malik ba. Annabi Muhammad (saw) Allah ya aiko mana. Shi kadai ne wanda binsa yake wajibi a Addini. Shi ne wanda in aka saba maganarsa da Sunnarsa to an aikata Bidi'a.
Wannan ya sa Malamai suka ce babu wani da ya zama wajaba a bi shi sai Manzon Allah (saw) kawai. Kuma duk wanda ya wajabta wa mutane bin wani mutum ba Manzon Allah (saw) ba to za a nemi ya tuba, in ya tuba Alhamdu lillah, in kuma ya ki, bayan an tsayar masa da hujja to za a tsayar masa da haddi.
Saboda haka Allah bai wajabta mana bin Imamu Malik ba, don haka in ya karhanta yin Azumin Sittu Shawwal, alhali Annabi (saw) ya kwadaitar a yi to maganar Annabi (saw) za mu bi ba maganar Imamu Malik ba.
Kuma babu inda Imamu Malik ya ce: Azumin Sittu Shawwal bidi'a ne. Wannar magana ba gaskiya ba ce.
Ta yaya Imamu Malik zai ce Azumin Sittu Shawwal bidi'a ne, alhali Hadisi ya tabbata Annabi (saw) ya ce: "Duk wanda ya yi Azumin Ramadhana, sa'annan ya bi bayansa da Azumin kwana shida a Shawwal kamar ya yi Azumin shekara guda ne"?!
Ta yaya Imamu Malik zai ce Azumin Sittu Shawwal bidi'a ne, alhali an ruwaito daga Magabata cikin Tabi'ai da na bayansu, irin su Hasanul Basariy da Ibnul Mubarak?!
Ta yaya Imamu Malik zai ce Azumin Sittu Shawwal bidi'a ne, alhali Mudarrif dan 'yar Imamu Malik, kuma Almajirinsa ya ruwaito cewa; shi kansa Imamu Malik din yana yin Azumin Sittu Shawwal din a kebance?!
Ta yaya mai bin Mazhabar Malikiyya zai ce Azumin Sittu Shawwal bidi'a ne, alhali ga nan manyan Malaman Mazhabar Malikiyya, irin su Imam Abu Muhamma Ibnu Abi Zaid Al-Qairawaniy (Mai littafin Risala), Ibnu AbdilBarr, Al-Bajiy da sauransu duk sun tabbaar da Sunnanci da Mustahabbancin Azumin?!
Saboda haka wannan salo da Dr. Gumi yake bi ba salo ne na ilimi ba, salo na ilmi shi ne ka yi bincike na ilimi a kan inganci ko rashin ingancin Hadisin, sannan ka tattara maganganun Malaman Muslunci a kan Azumin, sai ka ga matsayin Azumin, ba ka rike maganar Yahya bn Yahya Al-Laithiy guda daya tal, ka zo kana jingina wa Imamu Malik maganar da bai fada ba, ka zo kana haifar da rudani tsakanin al'ummar Musulmi.
Allah ya kyauta.
![](https://i.ytimg.com/vi/qFXZpy1GSQA/mqdefault.jpg)